RALIYA-20
.
Balarabe ya kama bishiyar ya hau" sannu a
hankali har ya kai reshen da akwatin yake"
Asabe tana kasa tana kallonshi" da zuwanshi
yakai hannu a tsorace ya jawo akwatin jingim da nauyi zuwa can sai yayi ta maza ya dora shi akan kirjinshi" yaga duk ya fara tsatsa saboda yawan laimar da ruwan da ya dade yana dukanshi" ga alama akwatin ya dade a saman bishiyar mutane basu sani ba
Balarabe ya sauko da akwatin kasa" Asabe tayi
saurin amsarshi taji shi da nauyi kamar an zuba duwatsu a ciki" nan da nan ta fara kici kicin budewa"
Balarabe dake tsaye a kanta yace da ita"
Bai kamata ki bude ba Asabe" mutumin da yayi
tsintuwa irin wannan kamata yayi yaje ya kaiwa
hukuma tukunna sai suyi bincike da kansu" Amma bai kamata mu rigasu budewa muga abinda yake ciki ba
Asabe taci gaba da saita tayoyin kwadon
akwatin" zuwa can ta danna mabudan dake a
kowane gefe nan da nan akwatin ta bude cikin
sauri tare da fitar da wani sauti kamar an balla
sillan kara" budewar akwatin keda wuya sai
Asabe ta kwantar dashi akan cinyarta dake wajen sannan ta bude murfin cikin sauri"
Balarabe dake tsaye yana kallonta yaja baya a
tsorace a sakamakon abinda ya gani a cikin
akwatin" ita kanta Asabe dake durkushe a gaban akwatin saida ta suma" ta bushe na dan wani lokaci" idanuwanta ko kiftawa basa yi zuwa can kuma saita dawo hayyacinta"
Bayan tahi ajiyar zuciya" balarabe yayi karfin hali ya matso kusa da matar shi Asabe" yana kallon Makudan kudin" dake cikin akwatin yace da ita a tsorace"
"yi sauri ki rufe Asabe kada wani yazo ya samemu da wadannan kudi mu jawowa kanmu
bala'i watakila ajiya wasu mutane sukazo sukayi a saman bishiyar" don Allah ki rufe in dauka in mayar dashi inda na daukoshi
Asabe ta harari mijinta balarabe cikin kankanin
lokaci idanunta sun canza kama" sun koma launin toka toka" yawanci idan ranta ya baci ko kuma idan zatayi wani wata doguwar masifa wacce zata kwana bata gaji ba" to daga idanuwanta balarabe yake ganewa" idan yaga sun canza launi" Asabe tace dashi a fusace
"Baza'a mayar din ba" sakaran banza ragon
maza kawai" in banda kai mahaukaci ne wa kake tsammanin zai tsinci akwati irin wannan cike da Dalolin Amurka yace zai mayar dasu inda ya dauko su?" wannan tsintuwa tawa ce" idan baka so" ni ina so
Balarabe ya sake matsowa kusa da ita a tsorace jikinshi yana tsima"
"kada kiyi haka Asabe" wannan ba karamin hadari bane muka tsinci kanmu a ciki" ki rufe akwatin nan" mu gudu mu bar wajen nan na fada maki wannan ajiya ce wasu sukayi" babu mamaki barayi ne kizo mu gudu kada suzo su same mu anan su karkashe mu
"Asabe tace da balarabe a fusace
"kayi tafiyarka kai kadai balarabe" daga yau
rabuwarmu tazo na fada maka" wannan akwati ta zama nawa" duk duniya babu mai rabani dashi ka "Sake ni kawai kayi tafiyarka ka koma gida na fasa zuwa unguwar da zaka kaini" dama wasu kudin zan je nema acan gashi kuma yanzu na same su anan
Balarabe yayi sauri ya waiga kowanne bangare
don ya tabbatar babu wanda yake ganinsu" babu kowa a dajin mutane basu fara zuwa gonakinsu ba
Asabe ta rufe akwatin cikin sauri" ta mike ta
kinkimeshi da kyar ta rungumeshi a kirjinta"
Duk da nauyinshi sai faman zufa take yi saboda tsananin rudewa da tayi da ganin wadannan milyoyin kudin tace da balarabe mijinta dake tsaye yana kallonta cikin fargaba
"kai nake jira balarabe" na fada ma cewar
rabuwarmu tazo bazan iya zama da kai ba a
halin yanzu babu maganar aure a tsakanina
dakai "saboda me Asabe?
Balarabe ya tambayeta a tsorace"
"saboda me?
"Asabe tayi murmushin ta na izgilanci tace
dashi "saboda yanzu ni miloniya ce" balarabe nafi karfinka" zama tsakanin miloniya da beran
masallaci bazai yiwu ba
Balarabe zai sake yi mata magana kenan" sai ta
murtuke fuskarta a fusace ta daka mashi tsawa "Ba na son wa'azinka balarabe kada ka bata mini lokaci" kayi sauri ka sallameni in tafi" kada ka jawo inci mutuncinka a dajin nan....."
Balarabe yaji duk da masifar Asabe yana sonta
baya son rabuwarsu" to amma kuma yaya zaiyi
da ranshi tunda dai ta matsa mashi dole saiya
saketa" bai san lokacin da ya fashe da kuka ba"
yace da ita
Shikenan Asabe" na sakeki saki daya" amma ina sonki" banso kiyimun haka ba" banso rabuwarmu dake ba"
Asabe tayi dariyar shekiyanci tace dashi"
"Sai wata rana mijina kada ka damu" nasan
bazaka taba mancewa dani ba a rayuwarka" bana bukatar kayan dakina" ka daukesu na bar maka kaci gaba da zama kai da momi kace mata Nina tafi sai watarana"
Asabe tayi saurin garzayawa cikin gudu-gudu
tana rike da akwatin tabar tsohon mijinta balarabe tsaye yana kallonta.." har tayi nisa sai ya daga murya yace da ita
Yanzu ina kika nufa Asabe" ina zaki je a cikin
dajin nan? Asabe bata waigo ba tace dashi tana sauri
Wurin zuwa ba mai wahala bane balarabe"
musamman idan kana da Milyoyin Kudi a tare
dakai kada ka dami nina san inda zanje sai
watarana...
Asabe tayi nisa balarabe yana tsaye yana
kallonta har ta bace ya daina ganinta
.
=======>******************<========
.
HAJIYA TABAWA ta fito daga cikin
fashashshiyar rumfarta inda take sayar da
abinci" wacce rufin kwanonta ya huhhuje kamar rariya" sai kadangaru da tsaka ke kai da komowa a jikin rumfar da kuma jirwayen ruwan sama na shekara da shekaru
Da fitowarta ta kalli kwastomominta dake a
Zazzaune akan benci wadanda yawancinsu
leburori ne" da kuma 'yan tasha sai kuma dan
abinda baza'a rasa ba na matafiya masu safara
suna kai kaya kasuwannin karkara Ganin wasu suna a zaune ba'a kawo musu abinci
ba" saita dakawa yaranta uku tsawa" karuwai
biyu da kuma dan daudu daya"
Nan da nan suka mayar da hankalinsu akan
uwargidansu ta tsaya a bakin rumfar shirim da
ita kamar bukka" 'yar gajeriya ce baka" mai
mulmulallen kai wacce ta matse shi da dankwali sai kace wani karamin tulu" sau da yawa bata tashi masifarta" sai taga kwastomomi sun hadu awajen" saboda tayi musu burga A san cewar ita ce babba" haka kawai sai ta fada karuwan da fada wasu lokutan hade da zagi" da yake tuntuni zuciyarsu ta mutu" kuma da yake tuni sun kaucewa tafarkin gaskiya na manzon tsira da aminci su tabbata agareshi" wannan
baya damun su" to amma kuma a boye idan sun kebe sukan dade suna gulmar mafadaciyar matar wacce take rike da su yau da gobe" tana neman arziki a tunaninta"
Shi dan daudun ba kasafai yake jin tsoronta ba"
da yake shine dan lelen ta" sau da yawa tafi
bashi amana fiye da karuwan yaran nata" domin kuwa ko ba komai takan sanar dashi wasu kadarorinta data saya" ta boye a gidanta
wadanda zasu taimaketa ako da yaushe" duk
lokacin da bukatar kudi ta taso mata"
Abubuwan da take bashi labarin ta saya ta boye sun hada da sarkokin daham masu tsada"
wadanda a yanzu haka a cewarta kudinsu sun kai kimanin Rabin miliyan kuma in banda
wadannan sarkoki da 'yan kunnaye da zobina
bata tanadi komai ba" a wannan sana'a ta dafa
abinci a bakin tashar mota" tun tsawon shekara
goma sha hudu da suka shude"
Ganin sun kura mata ido" suna jiran umarninta"
sai ta bude wagegiyar muryarta mai kama da
lasifikar garmaho tace dasu a fusace
me kuke yi kuka bar mutane a zaune baku basu
abinci ba? Daya daga cikin karuwan wacce suke ce mata Jiniya ta taso tana rangwada da siririn wuyan ta kamar na tsohuwar belbela" tasha damara da gyalenta kafarta babu takalmi" ta nufi inda daya daga cikin tukwane biyar din da ke kan wuta suna tiriri" ta bude daya da sauri ta jefar da murfin agefen murhun saboda zafi taja da baya" sannan ta ce wa uwargidan tasu Doya suke jira" kuma har yanzu bata karasa nuna ba Hajiya tabawa tace dasu
"Ai laifinku ne tuntuni naso ku fara dora doyar
nan to da yake ku bakwa jin magana sai
da kuka ga dama sannan kuka dora" gashi lokaci yayi har mutane sun fara tambaya ina amfanin wannan rashin mutuncin ace mutum yazo cin abinci sai yayi zaman jira
Ta dubi kwastomomin dake a zazzaune da jajayen idanunta" sannan ta washe wagegen bakinta wanda ke kama da barnar wuka" kuma wanda ke tona asirin shekarunta data dauka a baya tana kurbar barasa" kafin shari'a tazo ta daidaita sahun duk wani takadari dake zaune a birni da kewaye
Bayan ta gama tsorata kwastomominta da
abinta a tsammaninta za'a kirashi da murmushi
sai tace dasu "kuyi hankuri kada yanzun nan zata nuna" basu dora da wuri ba ne yau"
Kwastomomin da suke cin abinci suka dubi
wadanda ke a zaune suna jiran doyar" wasu
samari ne majiya karfi su uku wadanda da
ganinsu ko ba'ayi tambaya ba" idan mutum yayi
la'akari da tabon dake a fuskokinsu to zai iya
gane cewar in dai ba hadarin mota aka tabayi da su ba to babu shakka sunyi zaman daba" ko kuma yawon farauta" to amma kuma da'ace anan abin ya tsaya da anyi san barka" Lamarin rayuwarsu duk ya zarce nan a halin yanzu.
Hajiya tabawa ta dubi daya karuwar dake a zaune wacce ake cewa "Idon Gwal wata kakkaura ce wacce bata mori man canza fata na shafe-shafen zamani ba"
maimakon ta koma fara mai dan kyan gani" sai
tayi kala biyu" kamar zabuwa" wani sashi na
faffadar fuskarta dake kama da faranti" tayi fari
fegen idanunta kuma yayi duhu" da kuma wani
sashi na kunnuwanta
Duk da haka bata damu ba" domin kuwa mijinta
na bariki bai damu da ganinta a haka ba kullum
idan yayi kamasho a tasha ita yake fara zuwa ya zubewa kudin da ya samu" wani lokacin ta dauki wani abu ta bashi" wanda zai sayi taba da abinci" wani lokaci kuma idan taga dama saita hanashi ko sisi" kuma ta zazzagi iyayenshi har sai an bata hakuri saboda bai kawo mata kudi masu yawa ba" da zasu isheta cefane
Hajiya tabawa ta harareta" sannan tace da ita
"ke kuma kin zauna nan kina kallon mutane da
wadannan shegun tulu-tulun idanunta naki da ke kama dana mujiya" bazaki tashi ki taimake ta ku iza wutar a samu abincin ya nuna ba?"
Idon Gwal din ko kuma idon mujiya cewar
Hajiya tabawa mai abinci" ta taso cikin fushi.....
Tags
# Raliya
About Jamilu Ismail Muhammad
Soratemplates is a blogger resources site is a provider of high quality blogger template with premium looking layout and robust design. The main mission of templatesyard is to provide the best quality blogger templates.
Raliya
Category:
Raliya