RALIYA-21
.
Idon Gwal din ko kuma idan mujiya a cewar
tabawa mai abinci" ta taso cikin fushi ta nufi
inda 'yar fingililiyar kawarta take" suka taru suna iza wuta tare suka kalli juna suka yatsina fuska domin kuwa sun tsani wannan dunkulalliyar matar tana bada su a gaban kwastomomi baki" tana zaginsu don ta ga ita ce shugaba" to amma kuma da ace sun shirya sun zauna a dakunan aurensu domin raya sunnar fiyayyen halitta" anya kuwa irin wannan cin mutuncin zai same su?
Daga nan sai ta mayar da hankali akan dan
daudun yana zaune akan kujera ya juya musu
baya" yana fere kabewa ya kima wani katon zani akan shi kaya guda yana rangwada sannu ahankali yana rera wata waka ta garaya da yake
yawan cashewa da ita a duk lokacin da biki ya
tashi" aka gayyace shi hawa bori" tabawa tace
dashi "ke kuma idan kin gama wannan fera kabewar ki shigo ina son ganin ki zan aike ki wani wuri
"Gamsameman katon wanda zai iya kayar da
bajimin sa" ya lankwashe bayanshi bai waigo ba ya matse muryarshi kafin yace da ita cikin
girmamawa. "Gani nan zuwa idan na gama yaya.
Samari ukun dake jiran a sauke doya a cikin
kwastomomin suka harari dan daudun a lokaci
guda" su kadai suka san dalilin zuwansu wajen
wadannan gayyar tsiyar karuwai da 'yan daudu"
GARABASA. 4gb Data Kyauta Daga kamfanin AIRTEL
amma ba abinci ya kawo su ba.
Hajiya Tabawa ta koma cikin tsohuwar rumfar
kwanon inda take shimfida tabarma ta zauna da muhimman bakinta na sirri" wadanda ke zuwa kullum" yawancinsu tsofaffin bariki ne" da suke nemanta da kuma watsatstsun kawayen ta wadanda suka gujewa shiriya tun tali-tali
Bata dade da komawa cikin rumfar ba" kamar
daga sama sai ga wata bakuwa tazo wajen" ga
alama taci uban tafiya wujiya-wujiga da ita" duk
tayi zufa" tasha rana" amma kuma duk da haka
tana dauke da wani murgujejen akwati a
hannunta" da ganinta tafi kama da sababbin
shigowa bariki" ko kuma babu mamaki tsohuwar hannu ce
tayi canjin gari ne shine ta fado wajen sayar da
abinci" domin kuwa tasan cewar a irin wadannan wuraren suke samun helkwatar da za'a amshesu
Don haka kowa yayi tsammanin wannan katon
akwati dake a hannunta duk barazana ce babu
wata tsiya ke a cikin shi ba" sai 'yan
tsummokaranta na sawa da kayan kwalliya da
ba'a rasa mata dasu a jaka duk wuya"
"to amma kuma da ace wannan bakuwa zata dan bude akwatin ko kadan" kwastomomin da kuma karuwan su leka suga abinda ke a ciki" to da babu mamaki wasu zasu sume a wajen saboda tsananin kaduwa"
Bayan da bakuwar ta gaishesu sai tace kai tsaye "Nazo wajen Hajiya tabawa ne"
"Jiniya ta dago kai daga inda take a bakin
murhun tana hura wuta" duk hayaki ya cika mata idanu" tace da bakuwar"
"ki shiga cikin rumfar tana nan
Bakuwar ta shiga cikin rumfar dauke da katon
akwatin ta" wasu daga cikin kwastamomin sai
kallon hadarin kaji suke yi mata" domin kuwa
yawanci sun bada cewar ita ma ai 'yar zaman
kanta ce" wacce tazo neman taro da sisi daga
garin su"
"yan matan karuwan biyu da kuma dan daudun
suma a wulakance suke kallonta" domin kuwa
basu san a kawo musu wata bakuwa ta zauna acikinsu" Abinda duk wadannan mutane basu sani ba shine Wannan bakuwar wata tsohuwar aminiyar Hajiya tabawa ce" wacce suka dade da shakuwa tun awani yawon bariki da ya hadasu" kuma wannan akwatin dake a hannunta idan aka zazzaage
abinda ke a ciki zai iya samar da tituna da
makarantu da asibitoci da fanfuna da wutan
lantarki a duk fadin wannan karamar hukuma tasu
Gabaki daya mutanen sunyi mamaki da sukaji
Hajiya tabawa da ke a cikin rumfar ta taso cikin
farin ciki ta tarbi bakuwarta tana cewa cikin
Zumudi
"Ashe rai kanga rai Asabe?" sannu da zuwa
kawata" ashe kina nan a raye ina kika shiga
shekara da shekaru?" sannan kowacce ta kama
hannun kawarta suka tafa suna dariya da shewa
.
=====>+++++++++++++++++++<=====
.
Minti talatin bayan haka lokacin da doyar ta
karasa nuna aka zubawa samari ukun dake zaune suna jira sai suka fara kaiwa baki, hannu baka hannu kwarya. Suna cin abincin suna sauraren
duk wata hira da karuwan keyi da dan daudun"
Bayan sun gana an kawo musu ruwa" sai babban cikinsu wanda kuma ga alama shine jagoran tafiyar su yace da jiniya nawa ne kudin ku? tace dashi tana juya dan firirin wuyanta"
"dari biyu da arba'in ne
Saurayin yayi murmushi kafin ya ciro kudin ya
bata" ita a tsammaninta kwarkwasar da tayiwa
saurayin ya burgeshi" har yake yi mata fara'a
Abinda bata sani ba" shine siririn wuyanta da yagani shi ya tuno masa da wata mata da ya
darzama wuka a wuya wata uku da suka wuce"
lokacin da suka shiga gidanta yin fashi taki basu hadin kai" ta fito musu da gwal-gwalan da aka basu labarin ita ma ta boye a gidanta
Yanzu da saurayin ya kalli wuyan jiniya saiya fara tunanin abubuwan mamaki" itama tana bukatar wukar zuwa anjima da daddare"
Idan har suka shigo gidan Hajiya tabawa yin fashi da makami kamar yadda suka kudiri aniya ba wani dalili da yasa suka zo cin abinci awajen matar ba" sai don su fahimci yadda take gudanar da al'amuranta" da kuma lokacin da take tashi daga kasuwa ta koma gida"
wannan ya zame musu kamar al'ada duk lokacin da zasu je sata sai sun bi mutum sannu a hankali sun ga yadda yake gudanar da sha'anin rayuwarshi" sannan sai suyi mishi dirar mikiya idan dare yayi
Koda yake a tarihin wannan muguwar sana'a tasu basu yiwa maza sata" sai dai mata" domin kuwa sun fahimci mata sunfi maza bada hadin kai cikin sauri idan suka ga barayi"
sau da yawa bayan sun dawo daga sata idan
suka zauna sai su rika tuno abinda ya faru" su
duka ukun sun sha cewa! "mata basu da matsala da zaran ka nunawa mace bindiga zatayi sauri jikinta na rawa ta baka kudi da sarka" to amma kuma abinda yasha bamban a wurin maza" a da can kafin su fahimci haka" sun sha tsare hanya wasu mazan ko kashe su za'ayi bazasu taba fadin inda kudin suke ba" saboda tsabar taurin kai
Amma mace ko ido ka zare mata yanzun nan
Zaka sami sarka mai tsada kasa a cikin aljihu
kayi gaba abin ka ba wani wahala"
A wannan karon Hajiya tabawa itace sabuwar
wacce zata amshi bakuncin su" idan dare yayi"
an sanar dasu cewar matar tana da kudi sosai"
kuma bata yin ajiya a banki" don haka in gaskiya zasu gani anjima Domin kuwa duk da wannan jajayen idanu da take yiwa yaranta barazana dasu tana banbami" sun
san cewar da zarar sun nuna mata bindiga zata
lafa ta basu abinda suke so"
Domin kuwa su ba 'yan daudu bane da ta
rainasu da wuka suke wasa da bindigogi bada
ludayin miya ko askar fere doya da kabewa ba"
Jagoran samarin uku mai suna LADO NIGA ya
ciro kudin abincin ya bata" jiniya ta amsa tana
fari da busassun idanunta tace
"muna fatan wata tana zaku sake dawowa"
Lado yayi murmushi a zuciyarshi yace
"kada ki damu zaki sake ganinmu bada jimawa
ba Daga nan ya mike ragowar abokan tafiyashi su biyu suka tashi" akwai alamar dariya a fuskarsu da suka ji irin hirar da lado keyi da wannan bushashshiyar mata"
Daya a cikin su sunanshi BALA" daya kuma
sunanshi BANGIS" dukkansu karti ne majiya
karfi" wadanda iskar duniyar bushasha ta kado su wuri guda suka hadu suka zama abokan juna kuma masu yin sana'a daya
Bayan sun bar inda rumfar Hajiya tabawa ke
sayar da abinci da suka dan matsa nesa kadan"
sai suka zauna akan wani karfen injin birtsatsai
na ruwa" lado ya dubi bangis dake fuskantar shi ajere akan nasu karfen yace dasu
"Ina ganin bamu da wani haufi tana a gari babu
inda zata je yau" kawai mu dirar mata anjima"
Bangis yace dashi "musamman kuma naga kamar tayi bakuwa" ina jin koda yana da niyar fita zaiyi wahala ace bata dawo ba" komai dare"
Bala yace da bangis"
"Don tayi bakuwa wannan ba wata hujja bace da zaisa mu daga kafa" yau ko tana a gida ko kuma zata fita wani waje" baka ganin bakuwar ba" wata mai maiko bace" ina tsammanin irin
tsofaffin 'yan hannu ne data fara karewa shine ta sake gari" ta zo wajenta" wannan ba wata
bakuwar harkar arziki bace" kawai indai zamu
dira mu dira" kamar yadda mukayi niya"
Lado niga" yayi fito zuwa can yace
"mu dira kawai" komai ma muka samu yafi babu"
A haka dai mun rage na tabawa kafin wata
hanyar ta sake buduwa"
"sukayi dariya" a lokacin ne suka sake mayar da
hankalinsu acan inda rumfar matar take hayaki
ya turnuke a wani murhu Idon gwal ta duka tana faman fifita" a daidai lokacin ne kuma Hajiya tabawa suka fito ita da bakuwarta" tace da yaranta
"baku san idan kunga bakuwa tazo ku gaisheta
ba?"
wannan aminiya tace" mun dade bamu hadu ba"
sunanta Asabe ku dauki akwatinta ku rakata
gida tayi wanka ta huta kafin in dawo" tazo ne ta dan yi mani kwana uku kafin ta koma"
Karuwan biyu da gabjejen katon dan daudun suka zube cikin girmamawa suka gaishe da bakuwar"
sannan jiniya ta amshi akwatinta suka tafi gida"
Lado Niga da abokan tafiyarshi suka kawar da
kansu bayan matan biyun sun bace!"
.
=========************==========
.
'Dakin da aka sauke Asabe a gidan Hajiya
tabawa" yana cikin dakuna uku dake a jere da
juna" kuma dama ta tanade su ne musamman
don irin wannan ranar idan tayi baki" sauran
dakuna biyu inda yaranta uku ke kwana ne"
wadanda take cewa 'yan mata baki dayan su"
tare da shakiyin katon da ya mayar da kanshi
mace" saboda tsananin bala'in da ya fadowa
rayuwarshi a duniya
Wani abinda Hajiya tabawa ta kasa fahimta a
game da wannan ziyara da Asabe ta kawo mata shine" ganin yadda take faman nuku-nuku da katon akwatin da tazo dashi" sai kace ta ajiye wata tsiyar azo a gani a ciki"
to amma kuma bata tambayeta abinda ke ciki ba" tasan dai bai wuce tiramen zannuwa da tsofaffin takalma ba"
Hajiya tabawa ta dade da sanin Asabe tun a wani zaman sayar da abinci da tayi a cikin birni"
To amma kuma bambancin rayuwarta da kuma
Rayuwar Asabe shine ita tabawa ta dade da yin
murabus da sha'anin
Tags
# Raliya
About Jamilu Ismail Muhammad
Soratemplates is a blogger resources site is a provider of high quality blogger template with premium looking layout and robust design. The main mission of templatesyard is to provide the best quality blogger templates.
Raliya
Category:
Raliya