Gaskiya Dokin Karfe

Galadima.com.ng Domin sharhi kan al amuran yau da kullum

MURMUSHIN ALKAWARI-20
.
(m) Nazir Adan Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Kalima ta tsaya cak atsakar dakin kamar an soka mata kibiya ta riga tasan me sautin wayar ke nufi alamu ne da ke nuni da cewa sabon sakon wasika yazo awayar. Idan hara akwai abinda kalima ta tsana shine yan matan da a kullum sai sunyi masa sakon wasikar gaisuwa kokuma soyayya ta cikin waya.
Wace tsinanniyar ce kuma? Kalima ta tambaya a fusace lokaci guda kuma ta juyo zuwa inda salim yake zaune ta rankwafa akusa dashi. Suka fara karanta sakon dake kan fuskar wayar kamar haka:
..... NASAN BAKA SANNI BA AMMA NI NA DADE DA SANINKA DOMIN KAINE KESA ZUCIYATA FARI KAINE FITILAR IDANUNA ADA INA NESA DAKAI AMMA AYANZU INA DAF DA KAI ME YIWUWA MA KANA IYA JIN NUMFASHINA AKAN KYAKYKYAWAR FUSKARKA. NAN BADA DADEWA BA ZAKA ZAMA SARKI IN ZAMA SARAUNIYAR KA.... I CARE.
Nice FALMATA.
.
Shegiya tsinanniya kalima tace a fusace bakinta na rawa sannan saita warce wayar daga hannun salim cikin sauri ta daddana madannan wayar ta goge sakon wasikar sannan ta mika masa wayar tace tana huci tashi mu tafi. Salim ya dubeta cikin mamaki yace ina zamu? Kalima ta rike hannunsa ta kankame tace Inda zaka. Cikin mamaki salim ya sake dubanta yace.
Kikace kuma wankin kafa zaki. Kalima ta girgiza kai ta dada kankame hannunsa a tausashe.
Nafasa zuwa dakai zamu tafi inda zaka. Salim ya mayar da wayarsa aljihu sannan ya wuce gaba kalima tabishi abaya. Azuciyarsa yace YAU NA HADU DA JARABA.
.
HUDU 4
.
'Yaya kayi shiru? Cigaba mana baba sidi. Naji ka ambaci sunan mutumiyata falmata kana nufin kace har ta sauka a kano? Baba sidi ya yi murmushi sannan ya mike wuyansa kamar zakara yace.
Samo min ruwan sha Nas. Wannan tubanin duk ya mimmike min awuya cikin sauri na mike tsaye na zagaya bayan gidan sidi mai jaka na shiga wani shagon sayar da kaya dake daf da kasuwa na sayo jakar ruwa biyar cikin sauri na dawo na ajiye ledojin ruwan agabansa azuciyata ina ta tunanin zuwan falmata kano.
Sidi mai jaka ya dauki jakar ruwan daya yasa tsofaffin hakoransa ya huda ledar sannan yasa abaki Ja daya ya zuke ruwan ya jefar da ledar kana ya sake daukar ledar ruwa ta biyu ya zuke sannu ahankali ya zuke guda hudu sannan ya dubeni yace.
Wani lokacin tubani ba ruwa hadarine bakaji yadda suka tokare min kirji ba kamar na hadiyi tabare. Na bushe da dariya nace.
Ai kana kokari ma baba sidi dan ni da tubani saidai daga nesa nesa sidi mai jaka ya girgiza kai.
Kaga kuwa ba karamar asara kakeyi ba rashin cin tubanin nan don baka san dadin da nakeji bane shiyasa kullum nayima tayi bakasan ci.
Wata rana zanyi kokari na gwada cin kwaya daya nace dashi duk kuwa da cewa nasan abu ne mai wuya. Sidi mai jaka yayi kamar ya dauki ragowar jakar ledar ruwan sanyi data rage ya shanye can dai saiwata zuciyar tace ya bari tukunna sai anjima. Maimakon haka sai ya dauki tubani guda ya jefa abaki ya dubeni.
Nas gashi dai har Allah ya kawo mu karshen zarurrukan labarinmu guda uku kuma yanzun nan zan kulluma su guri guda. Ya danyi shiru.
Ina fatan kana biye dani. Na gyada kai.
Sidi mai jaka ya gyara zama yace bari to mu fara kulla zararrukan labarin guri guda. Sannan sai yaci gaba.
.
Acikin wani kayataccen madaidaicin daki a Ni'ima hotel dake nan kanon dabo falmata ce kwance akan gado wayar ta tafi da gidanka ahannunta tana danne danne cikin murmushi daga inda take kwance takan jiyo sautukan jaruman fim din dakee daukar shirin fim acikin otal din. Tun sa'ar data sauka a otal din kwanaki biyar da suka shude ta sami labarin cewa jaruman zasu zo otal din daukar shirin fim acikinsu harda jaruminta SALIM.
Ranar lahadin data baro garin borno ta shigo kano karfe uku na dare dauke da katuwar jakarta. Dan kabu kabun daya dauketa ne ya kaita ni'ima otal sakamakon tambayarsa da tayi na ya kaita wata kebantacciyar otal mai kyau.
Lokacin da kan kabu kabun ya sauketa saita zaro naira dari biyar ta mika masa dan kabu kabun yayi kokarin yabata canji saita girgiza kai ta haske shi da murmushin alkawarinta tace.
Kabar shi kawai... Na gode ta juya ahankali tana rausaya kamar bishiyar turare lokacin iskar damina ta nufi wajen karbar baki.
Dan kabu kabun yabita da kallo har saidata bace sannan ya girgiza kai sannan ya tuka babur dinsa cikin farin ciki ya tafi abinsa murmushin datayi masa yafi kudin data bashi faranta ransa azuciyarsa yace. Matar wani bata wani ba.
Washegarin ranar da safe falmata ta dauke shatar mota tace da direban ya kaita inda ake cankin kudin kasashen waje direban bai tsaya da ita ako ina ba sai a wafa fagge falmata ta canza kudi na akalla naira dubu dari uku sannan direban tasi din ya daukota akan hanyarsu ta dawowa falmata ta sayi jaridu akalla kala bakwai bayan data dawo dakinta ta kwanta saita fara bin jaridun daya bayan daya tana karantawa har ta gama bataga wani labari daya keda alakar mutuwar mijinta ba. Kuma har wannan rana ta juma'a da take kwance akan gadon wayarta ahannu tana kokarin turawa abin kaunarta salim sako na biyu babu wata jarda data buga labarin mutuwar mijinta.
Falmata ta sauko daga kan gadon sa'ar data.