Gaskiya Dokin Karfe

Galadima.com.ng Domin sharhi kan al amuran yau da kullum

RALIYA 07

RALIYA-07
.
Yan Makaranta An Dawo Ne?
"RALIYA ta gaisheshi cikin ladabi ya
amsa" ganin tana ta fama da katuwar akwatin sai ya mayar
mata ya dora akan amalanken ya tura
mata"
Raliya tayi mashi godiya tabi shi a
baya" suna ta
sauri" suna wuce manoma a gonakin
dawa da
masara" suna ta faman aiki" Raliya
taso ace ta
rage kudi a hannunta data ba
mutumin ko naira
ashirin ne" domin kuwa ya taimaka
mata wajen
daukar mata wannan akwati mai
nauyin tsiya" to
amma kuma bata da sauran ko
kwabo a
hannunta" su kenan ta bada su kudin
mota" to
saidai kuma da ace raliya zata
bude akwatin da
mutumin ke tura mata data sami
kudin da xata
bashi lada masu yawa"
Abin da raliya da mutumin basu
sani ba" shine
wannan akwatin dake gabansu ba
tsummokara da
littatafai bane a cikin shi" Dalar
amurka ne har
kimanin miliyan hamsin"
.
=====>******^*******<=====
.
FARAR motar tana cikin tafiya da
fasinjojinta
guda shida sunyi shiru" ba zato da
tsammani sai
suka ji jiniyar motar 'yan sanda a
bayansu"
direban ya kalli madubin motar yaga
bakar motar
yan sanda ta cika Fal da kwalawa
suna rike da
bindigogi" nan da nan ya rage gudu
daya ga 'yan
sandan suna tsayar dashi"
Tsayawar motar keda wuya" sai
motar 'yan
sandan taci taya a bayanta" 'yan
sanda shida
suka firfito a gurguje suka xagaye
motar suna
xare idanu" Jarmai dake xaune yayi
mutuwar
tsohuwa domin kuwa yasan cewar
asirinshi ya
tonu" shiyasa suka biyoshi"
Yaron motar ya bude kofar motar"
'yan sanda
suka leka ciki biyu daga ciki suka
cakumo Jarmai kamar dan wake a lokacin ne
wani dan
sanda ya bude bayan motar ya
sungumo akwatin
ya kankame ta yana ta baraxana da
bindigar dake
a hannunshi" wani a cikin 'yan sanda
ya dakawa Jarmai tsawa"
"wannan shine akwatin?"
Jarmai ya girgixa kai "yace shine"
'dan sandan
yasa gindin bindiga ya kwada mishi a
gepen
bakinshi" hakora uku suka yi tsalle
suka fito
waje" wata mace dake a cikin motar
ta rusa
kururuwa"
Jarmai ya xube kasa yana shure
shure" jini yana
kwararowa ta bakinshi da hancinshi"
nan da nan
suka tattarashi suka hada da kawatin
suka nufi
cikin motarsu" ba laifin su bane"
domin kuwa tun
cikin daren an basu umarni in har
sunga Jarmai
kada suxo dashi da kamanninshi" su
canxa mashi
halitta yadda ko uwarshi ta ganshi
baxata iya
ganeshi ba"
To amma kuma har 'yan sandan suka
ja motarsu
sukayi kwana suka tafi bata Jarmai
suke yi ba
da yake kwance magashiya" ta
akwatin kudin
suke yi dake a tsakiyar su" domin
kuwa su kansu
basu yarda da junansu ba" suna jin
tsoron kada
wani a cikinsu ya harbesu ya gudu
da miliyoyin
kudin shi kadai"
Da ace xasuyi karambanin bude
akwatin da
sunsha mamaki domin kuwa xasuyi
nasarar
tsintuwar littatafan karatu da kuma
rigunan
mama da tsofaffin takalma
.
=======>*****^*****<======
.
Kauyen dan marke wanda yake da
nisan kilomita
daya da rabi daga bakin titi" yana
cikin karamar
hukumar garun malam" dake a jihar
kano" dan
marke kauye ne dake da dimbin tarihi
domin
kuwa akwai tsofaffin dake a raye a
cikinshi"
wadanda suke ba yara tarihin kafuwar
wannan
kauye" tun xamanin mulkin mallakar
turawar
ingila" kafin a sami yancin kai"
ALLAH ya albarkaci kauyen dan
marke da
manyan manoma na rani da kuma na
damina"
kusan a kowanne yanayi mutum ya
shiga cikin
kauyen da wahala ya sami mutane a
xube suna
xaune" koda yaushe mutane suna
gonaki da kuma
fadamu"
Akwai kuma masu xuwa kamun kifi"
domin kuwa
a xagaye da kauyen dan marke
manyan koguna ne da ba'a taba ganin sun kafe ba atarihin da za'a iya tunawa"
Kasancewar yankin karkarar da
kauyen dan
marke kewaye yake akwai yalwatacciyar
ciyawa a gepen
fadamu rani da damina" shiyasa
fulani suka kafa
rigaye jefi-jefi a kusa da kauyen"
wannan ya sake
taimakawa maxauna yanki yajen
samun isassun
dabbobi da kuma samun takin
gargajiya da arahar nono da man shanu"
.
Duk da wannan albarka da ubangiji
yayiwa yankin
karkarar na samun abubuwan dogaro
da kai"
hakan bai hana samun matasan dake
xaman
kashe wando ba" tun sape har xuwa
dare" naziru yana daya daga cikin irin
wadannan
hatsabiban matasa majiya karfi dake
a kauyen
dan marke" wadanda sau daya idan za'a yi fada
tsakanin fulani" makiyaya da kuma
manoman
kauyen dan marke su Naziru ake
sawa a gaba"
suyi ta ife-ife da makamai a hannu"
domin kuwa
duk cikin samarin dake wannan
kauye babu
wanda ya kama kafar Naziru " wajen
hatsabibanci da kuma son tada
xaune tsaye"
Mahaifinshi malam muntari shine
ladanin dake
kiran sallah a kauyen" sannan kuma
shine na'ibin
babban limamnin dake yankin
karkarar" kowa
yana ganin mutuncinshi badon halin
'ya'yanshi
biyu sun bayar da shi ba"
Malam Muntari shine mahaifin
Naziru da kuma raliya 'yar makaranta" da
Naziru da
kanwarsa raliya sunyi matukar yin
kaurin suna
a wannan gari nasu" Naziru yayi
bakin jini ne
badon komai ba saboda kowa yana
da labarin
baya xuwa gona domin taya
mahaifinshi aiki".
Sannan kuma jifa-jifa na cewa wai ya
fara shan taba" a tarihin kauyen dan marke ba a taba samun wani saurayi da ya taso yasha taba ba sai akan NAZIRU"
.
Yawancin matan garin har gargadin 'ya'yansu
sukeyi idan sun dora masu talla" ko Naziru ya
kirasu zai saya kada su sayar mashi" suce an
hanasu"
Akwai wata mata dake dorawa 'yarta tallar tubani
da manja" wacce Naziru ya kira yarinyar ta ya
sayi kwano biyu" da matar ta sami labari" da
kyar makwabta suka xo suka cece yarinyar"
matar tana ta jibgarta tana cewa"
"kullum idan zata fita saina ja mata kunne" ko
hanya ta biyo taga Naziru tayi sauri ta shige
wani gidan sai ya wuce" amma shine ya kirata
taje har ya sayi tubani ya taba min kwano"
Ance saida matar tayi kwana bakwai tana wanke
kwanonin da tokar makaranta da kuma kasar
masallaci kafin a sake xuba abinci a ciki" saboda
Naziru mai shan taba ya taba kwanonin da
hannunshi"
.
Ita kuma RALIYA an tsaneta ne a garin saboda
tayi shirgegiya amma kuma mahaifinta yaki aurar
da ita" tsararrakinta sun haifi 'ya'ya hudu xuwa
biyar" shiyasa da xarar ta dawo hutun makaranta
matan garin xasuyi ta gulmace-gulmace"
wadansu suna cewa ai anji labarin tana da
wannan ciwon na kanjamau da ake kwasowa a
birni"
wadansu kuma sunce duk wata sai an xubar
mata da cikin shege"
To amma kuma a bangaren malam muntari"
shidai yasan hakika yana da matsala babba a
bangaren danshi Naziru" kuma shidin ma ba'a
xaune yake ba" duk sati sai ya sa an sauke mashi Ashafa" sannan kuma yana da wata bara daya sa
ana rubuta mishi ita kafa saba'in duk karshen
wata yana tsare Naziru yana sha domin a samu
ya daina wannan lalata da ya sawa kanshi" ta
barin suma akai da kuma shaye-shaye da xuwa
bakin rapi suna yin karta shi da lalatattun
abokanshi"
Sannan kuma malam muntari ya sami wani
lakani a wajen wani bafillatani wande ake
barbadawa a tsire aba yaro ya cinye tsiren a
xaune" a cewar bafillatanin komai ibilishin da
yaro ya xama indai aka barbada garin sau biyu"
to an sami sauki har abada" sai ya koma waliyyi"
Malam muntari ya barbada wannan magani a
tsinkayen tsire yafi sau goma koda yaushe ya
kira
danshi Naziru saiya zare mishi idanu yace ya
xauna ya cinye tsiren"
to amma kuma har yanxun babu alamar nadama"
Naziru sai kara gaba yake yi" maimakon yayi dan
dama dama" ko sati biyu ba'a yi ba ya saci wata
tunkiya tun daga lokacin malam muntari ya fara
karaya da lamarin Naziru domin kuwa
hatsabibancin shi ya wuce duk inda ake
tsammani"
To amma kuma a game da raliya yarshi
wannan
sai dai ayi mashi sam barka" domin kuwa bai
taba kamata da wani laifi da zaice mata tir ba" ta
tsare mutuncinta tana karatunta" kafin ta
kammala kuma ta fito da masoyinta ayi mata
aure"
A ka'ida a kowacce safiya idan an tafi gona"
Naziru tare da shakiyan abokansa su SHEGEN
SAMA basu da wani aiki saisu nufi bakin kogin
dake bayan garin su xauna a gindin wani
mangwaro su nada mandula su sha suyi karta"
kamar kullum a karon bayan duk mutane sun tafi
gona" sai Naziru ya hau tsohon babur dinshi
(SUZUKI) wanda ya taba yin gobara ya kone"
idan zai tada babur din saiya xungura shi a guje
sannan sai yayi tsalle ya haye" gashi kuma babur
din bashi da salansa idan ya fara burari sai yaran
kauyen suyi ta koke-koke" wasu kuma suna
shigewa gida a guje" domin kuwa kafin a saba da
babur din a lokacin da Naziru ya fara tadashi a
kauyen mata duk suka bi suka rude suna salati"
sun dauka cewar girgixar kasa ake yi"
NAZIRU ya xungura babur din a guje yayi tsalle
yasa giya" amma kuma a wannan karon baici
sa'a ba" haka yayi ta dama dashi har yakai bakin
kogin" yana sanye da kodadden wandonshi na
sojoji daya fashe a gwiwa" da kuma bakar riga
wacce ta dauki shekara biyu bata ga ruwa ba" in aka dauke ruwan saman da ya jikata bara" Naziru
bazai taba mancewa da wannan rigar ba" domin
kuwa a caca ya ciwota tare da wani takalmi"
Bayan yaje bakin kogin bai iske abokan
shekiyancin shi ba" sai yayi fushi ya gunguro
babur din ya kamo hanyar dawowa gida" yana
cikin gungura babur din" sai kuma wata xuciyar
ta raya mashi cewar ya sake jarraba tayar dashi
me yiyuwa yaci sa'a ta tashi"
Naziru ya ingixa tsohon babur din a guje" sannan
yayi tsalle yahau yasa giya" babur din ya sarke
da ihu" saida tsaunukan garin suka amsa kuwwa"
sannan ya cilla da shi a guje Naziru ya nufi gida
yana murxa babur din"
A daidai lokacin da yake kan tafiya ne kafin
yasha
kwana ya shiga garin" wasu bakin mata tsofaffi
sun biyo ta hanyar xasu nufi wani kauye" suna
tafiya suna labarin jirgin da suka sami labari ya
fado a birnin kano a watan da ya wuce" wanda
ya kone gidaje da mutane bil adadin" sai kuma
sukaji rugugin wani abu ya tunkarosu kamar zai tsaga kasa"
saboda tsananin burari nan da nan tsofaffin
matan suka juya cikin kauyen a guje domin kuwa
sun dauka cewar jirgin ne irin wanda suke jin
labarin ya fado a kauyen a halin yanxu"
Matan suka watsar da kullin kayayyakin su