Gaskiya Dokin Karfe

Galadima.com.ng Domin sharhi kan al amuran yau da kullum

Showing posts with label Tsegumi. Show all posts
Showing posts with label Tsegumi. Show all posts

TSEGUMI 16 Karshe

TSEGUMI-16
.
KARSHE
.
Dariya ta kamayi amma duk da haka idanunta 'kyar a kaina bata ko 'kiftasu
"Ya akai kasan ni na daukesu?"
"Taya bazan sani ba"
"Lallai dagaske kai 'din KARSHE ne"
"Wato da farko ban kawo a kaina ke din bace sai daga baya na ankare. Na sani lokacin kinzo d'aukar hotonki ne shine kika had'a dasu don 'badda tunanina."
"Kasan lokacin da na fara ankarewa da binciken da kakeyi game dani,zuciyata ta rayamin cewa kana da hotona a wajenka wanda ka d'aukeni a tattaunawarmu shine nazo na dauke"
"Bakyaso na buga hotonki a jaridar don kar Jaheed ko wani daga cikin mutanensa su gani ko?"
Girgiza kanta kawai tayi alamar eh
"Wai kuwa na tambayeki man"
"Fad'I tambayarka"
"Amma dai kina karanta littatafan hausa musamman irin na Nazir Adam Salih ko?"
"A'a me ka gani?"
"Kawai naga wasu abubuwa shigen rubutunsa tattare dake"
Hannuna na le'ka agogona 'karfe biyu daidai na dare (02:00a.m) waiyo Allah nace a raina har yanzu dai ban samu wata mafita ba. 'Dago kaina na sake yi ina kallonta har yanzu babu alamar sassauchi a tattare da ita. Ganin zata iya harbina kowanne lokaci idan taji shirun yayi yawa ne yasa na sake 'daukan wani layin.
"Farkon wajen da na fara gano kece ainashin matar Jaheed shine lokacinda na tsinci wasikar da kika aikowa Abubakar a gidansa. Wato sai yanzu na yarda da abinda wasu mutanen ke fada"
"Me mutanen ke cewa"
"Sunce kaji tsoron macen da ta had'a abubuwa biyu"
"Me da me?"
"Kyau da kuma hikima"
"Hmm taya akai ka tsinci wasikar?"
"A dakinsa daya rushe,a cikin wata tsohuwar dirowa"
"Yanzu ina wasikar take?"
"Tana gida"
Yanzu kam na tabbata duk abinda zan fada na fadesu,sai dai har yanzu ban shiryawa mutuwar ba hakanne tasa na 'dora da cewa
"Na 'kara tambayarki?"
"Ina jinka"
"Kin yarda yanzu cewa kece Hadiza Abdullahi Adamri,Fatim matar Jaheed Auwal ba Jamila ba?"
"A'a"
"Me yasa"
"Saboda har yanzu ban gamsu ba kawai dai ka ja dogon labarin mai rikitarwa wanda ba kowane zai gamsu dashi ba"
"Idan kina musu me zai hana muje kotu muji ko Alkalin zai 'ki gamsuwa"
"Na fadama babu wani kotu da zaka daya wuce nan,kuma yanzunnan wannan kotun zata yanke ma hukunci"
"Kamar yadda ta yankewa Abubakar?"
"Yauwa eh"
Akwai kuma wani abu da nake son na sani"
"Menene?"
"Saboda tsabar wayonki kika yaudari Jaheed Auwal ya aureki sannan kika samawa kanki kyakkyawan mazauni a zuciyarsa saboda tsabar kissa,amma me yasa kika kasa fahimatar cewa idan kina tare dashi zaki mallaki makudan kudade fiye da miliyan goman da kika cuceshi?"
"Kasan kuwa yadda mutum yake ji idan yana tare da mutumin da bayaso a matsayin abokin rayuwa?
Shiru kawai nayi na zuba mata ido,lokaci guda naji wani tunani yazo min wanda na tabbata zai kubutar dani!!
Shiru kawai nayi na zuba mata ido,lokaci guda naji wani tunani yazo min wanda na tabbata zai kubutar dani,ban jira ba kuwa na fara gabatar da shi kamar haka
"Kin san cewa a bincikena da nakeyi a kanki sai da na gano cewa ke........."Shiru nayi lokaci guda na kauda idona daga nata na 'kurama 'kofar dake bayanta ido. Idanuna na zazzaro cike da firgici kai kace wani dodo na gani wanda ke 'ko'karin kunno kai cikin 'dakin. Dagangan nayi hakan saboda burina ta kauda idonta daga gareni koda kuwa na 'yan sakanni ne,cikin sa'a kuwa ta fad'a tarkona. Juyawa tayi da niyyar duba abinda na gani a bayanta,cikin 'kiftawa kafin ta dawo da dubanta gareni na daka tsalle na fad'a ta tagar da ke kusa dani jikake timmm na fad'a waje. Ai kuwa ban jima da kaiwa 'kasa ta biyoni aguje tana harbi ba 'kak'kautawa. Da gaggawa na mike sannan na fake a jikin lungu na bangon dakin daga waje,bindigata na zaro nima na harba cikin dakin ba tare da sanin wajen da na harba ba.
Gaba 'daya dakinne ya kaure da duhu,ashe dai harbinda nayi ne na samu 'kwan lantarkin da ke ci a dakin. Karar takun sawunta naji alamar tana fitowa hakan tasa na arce a na kare,kwane-kwan
e na ringa yi a yayinda nake gudun daga wannan sashe zuwa wannan. Ganain haka yasa itama ta ringa aikomin da sakon harsashi kowanne bangare ba 'ka'k'kautawa. Banyi nisa ba cikin gudun da nakeyi naji saukar harsashi a kafata,hakan tasa na saki wani uban gunji mai 'karfi na fad'I kasa shame-shame a yayinda ita kuma ta tunkaro ni gadan-gadan.
Tsakaninta dani bai wuce taku hamsin ba najiyo wani sauti daga can nesa ana fadin "waye anan"da alama sautin ta microphone yake fitowa. Ai kuwa bata jira ba ta aika da sakon harbi daidai wajenda muka jiyo sautin muryar,faruwar hakan ke da wuya daga can bangarenma naji sun sako tasu wutar na dan wani lokaci kafin daga bisani a tsagaita. "Su waye kuma wadannan?Ko dai 'yan sanda ne?"Na tambayi kaina. Ni dai ina daga 'kasa kwance cikin jini sai naji dayan na cewa kofur ku 'karaso nan mun harbeshi,jira nake naji sun yanyameni amma ga mamakina sai naga dukansu sun nufi wajen gidan,sai a sannan na hango ta kwance a 'kasa sakamakon haskata da sukayi da fitulunsu masu tsananin haske.
"To amma me wannan mutumin ke harbi tun farko?"Naji dan sandan yace da 'yan uwannasa
"Gaskiya duk yadda akai yana da abokin karan battar"inji dayan
"Mu bincika ko zamu ganshi 'kila shima an kashe shi ko kuma ya buya a wani wajen"
"Gani nan anan"nace dasu da 'karfi a lokacinda naji sun fadi haka sannan na dora "kar ku harbeni,so take ta kasheni"
Shiru ne ya biyo baya,can sai dayansu yayi magana "waye kai,kuma me ke faruwa anan?"
"Sunana Haidar Ali ni dan jarida ne"
"Haidar kaine?"Aka ce dani,naso na shaida mai muryar amma na kasa
"Eh nine"
"Kana ina?"
"Gani nan anan"
"Fito fili mu ganka"
Dakyar cikin jan 'kafa na taso daga inda nake kwance,amma kafinnan sai da na boye bindigata a 'kuguna.
"Haidar me kakeyi anan?"
Daga kaina nayi na kalli mai tambayar tawa sai a sannan na ganeshi,abokinn
annawa ne da ya aramin finger print gadget
"Ta mutu ne?"Nace dashi
"Wacece?"
"Matar dake kwance a 'kasa"
"Ai ba mace bace Haidar ko baka ga gemu ba a fuskarsa?"
"Ba namiji bane macece badda bami ne wannan gemun da kake gani"nace dasu
Sai da suka matsa har kusa da ita sannan suka fisge gemun da ta saka sannan suka tabbatar da abinda na fadamusu.
"Taya akai kuka san muna nan?"
"Mun dawo daga operation ne sai muka ga mota a gefen titi ganin haka yasa muka tsaya bincikawa sai kuma muka jiyo 'karar bindiga".
<<<<<<<<<<
Washe gari dana farka sai na tsinci kaina kwance a gadon asibiti gefena nurse ce a zaune.
"An ciremin harsashin?"
"A'a amma yanzu za'a cire ka huta tukun"
Bayan kamar awa guda da ciremin harsashin budurwata A'isha da abokin aikina Ibrahim suka shigo dakin da aka kwantar ni
"Ya jikin naka?"Tace dani
"Da sauki"
"Yanzu abokina sai da binciko wannan lamarin?"
Murmushi kawai namar bance 'kala ba sai a sannan na tuna wani abu yau ne daidai ya cika kwanaki goma sha hudun da Jaheed ya yanke min. Ina cikin wannan tunani kuma sai ga maigidanmu Ibrahim Atiku ya shigo shima yana ta washe baki
Cikin isa da gadara na dubeshi nace "Atiku so nake ka samomin lambar da zata sadani da Jaheed yanzu" "Ba damuwa"yace dani sannan ya fita.
.
KARSHEN TSEGUMIN KENAN.
.
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH

TSEGUMI 15

TSEGUMI-15
.
"Kamar yadda na fad'amiki ina da hujjoji 'kwarara wanda zasu gamsar da kowaye wanda zan kawo miki su 'daya bayan 'daya. Amma kafinnan zanso na gama baki labarin"shiru nayi ina kallonata ko zatace wani abu kafin naci gaba amma batace 'kala ba
"Yauwa bayan kun samu wadannan kudaden keda Abubakar da shekara guda shine kuka gina wannan gidan sha'katawar. Da farko tsarin zamantakewarki da Abubakar tana tafiya daidai kafin daga baya ya fara kawo tsoffin abokansa Club d'in wanda ke kuma tsoron kada su ganki su shaidaki shine kika yanke shawarar garga'darsa akan ya daina amma ya'ki har ma yake miki barazanar zai fasa 'kwan kowa yaji. Kin tsorata sosai da barazanar da ya miki,bayan kunyi aure shine kika shammaceshi kika taho dashi nan gidan gonar kika kasheshi. Na tabbata 'kwarangwal 'din da ke cikin akwatinnan nasa ne,ko ba haka bane?"
"Wannan shine kawai hujjar taka?"
"A'a,ai na fad'amiki labarin nada tsayi zan fad'amiki komai,a bincikena akan Abubakar an fad'amin cewa ma'aikatanki kin fadamusu mijinki ya mutu sanadiyyar nutsewa da jirginsu yayi kamar dai yadda kika fadamin a tattaunawarmu amma ban yarda ba,sai kuma na tuna lokacinda nake tambayarki abinda kike sha'awa kikace noma shima ban yarda ba amma da na had'u da Hajiya Jummai (mari'kiyarsu)sai take fadamin kina sha'awar noma da shuke-shuke. Lokacinda yaronki ya fadamin cewa kina da gidan gona kuma harda daki a ciki a wajenn gari na tabbatarwa da kaina cewa anan kika kashe Abubakar. Kinyi 'ko'kari wajen 'badda hankalin duk wani mutum da zaiyi 'ko'karin tona asirinki,babu shakka nima na yaba kaifin basirarki"
"Kana 'batamin lokaci fa,duk abubuwannan da ka fada babu wanda zai gamsar da wani cewa nice Hadiza Abdullahi Adamri ko Fatima Jaheed ko kasancewata 'yan biyu da har za'a gamsu cewa masauyen 'yar uwata nayi a madadina"
"Kar ki damu zan gamsar dake yanzu,ki saurareni kiji. A tattaunawarmu dake kin fadamin cewa asalin garin mahaifinki Busuku ne,naje har garin domin tabbatar da haka daga nan kuma sai na dawo kano au kafin na dawo kano sai da na biya ta kakori garinsu Abubakar inda na hadu da mahaifinsa yake fadamin irin munanan halayyansa sai naga sun sa'ba da yadda kika fadamin gameda shi. Da na dawo kano sai naje gidan yayansa wanda shima ya tabbatar min munanan 'dabi'unsa da yadda ya sama masa aiki a kamfanin takalma amma aka koreshi saboda halinsa. A can ma'aikatar ne na samu sunayen mutanen da ke kawo masa ziyara ciki harda ke (Hadiza Abdullahi Adamri)tun daga wannan lokacin na fara bincike a kanki har restaurant 'dinda kika had'u da Jaheed. A wata farar mota 'kirar BMW yazo ya daukeki,nasan zakiyi mamakin yadda akai nasan haka. Akwai wani mai shago da take da dabi'ar rubuta lambobin duk wata mota data birgeshi,agunsana samu lambar motar inda aka tabbatar min da cewa ta Jaheed ce
"Dakyau! Sai dai har yanzu banji wata hujja mai 'kwari ba"
"Daga nan kuma sai na binciki makarantar da kikayi,anan na fara gano cewa ku 'yan biyu ne sannan na samu adreshin Hajiya Jummai itace ta tabbatar da kamannin da kukayi da juna"
"Sai kwana kake har yanzu ka kasa fadin wani abu mai 'kwari"
"Nayi 'kokarin samun hoton Zainab,jiya kuma na sami naki a gidan Jaheed. Bayan na dawo don gano wani bambanci tsakaninku da juna ne na gano cewa akwai 'dison baki a kunnenki dan karami sabanin Zainab"
Dariya ta kamayi ba 'kak'kautawa sai dai bata kauda idonta a kaina ba
"Menene abin dariya kuma anan"
"Wallahi kai gara ne,yanzu wannan shine hujjar da ka rike?"
"Tsaya kiji"
"Ya isheka haka"
"Ina da wata hujjar"
"Wacce hujja kuma kake da ita?"
"Jiya lokacinda nake gidan Jaheed kafin na fita sai da na gwada tamabarin hoton hannun gawar (finger prints)sannan na dauki wasu kwalaben turare da kikayi amfani dasu suma na gwada amma basuyi daidai dana gawar ba. Da yammannan yau nazo Club dinki na dauki hoton naki yatsun ta hanyar yaudararki ki rikemin kwalba sanda nake nuna miki kamar 'kwaro ya fada a ido na. Nayi sa'a lokacin kanki a kulle yake baki gano plan 'dina ba har na samu kika rike kwalbar. A gida dana gwada sai naga sunyi matching dana sauran kwalaben da kuma agogon da na tsinta a motar da kike bibiyata. "
"Wannan tsinannen,mummunan mutuminnan sai naga bayansa wallahi sannan na kone gidan idan yaso naga ta inda har wani zai samu wasu kayaki da nayi amfani dasu"a fusace cike da 'karaji take fadin hakan,da alama ta fusata da yadda Jaheed din ya adana kayakinnata.
"Kinga dakata,duk wannan bazai kaiki ko ina ba. Me yasa don Allah zaki kashe 'yar uwarki jini 'daya.Saboda wata bukata taki anan duniya?"
"To menene amfaninta,yarinyar da bata da wani bambanci da karuwa,idan ka dauke iskanci da batawa mutane suna mai ta sani. Ko kadan bana takaicin abin da na mata"
"To ke fa? Kina ganin a hakan gara ke?"
"Kwarai kuwa"
"Naji amma waya baki damar daukan doka a hannunki alhalin ke ba hukuma ba?"
"Kaga kar kamin wa'azi"
"Naji amma me yasa zaki kasheta saboda kudi?Ina kike tunanin kudin zasu kaiki? Kin aikata 'barna da dama,ko kinsan adadin mutanen da kika hallaka sanadiyyar haka? Bari na 'kirga miki su. Da farko kin kashe mijinki Abubakar wannan ne ma ya tunamin da wani abu,babu shakka duk fadin 'kasarnan ke ce mace ta farko da ta taba aikata Polyandry"
"Menene Polyandry?"
"Ma'ana mace ta auri sama da miji daya a lokaci guda. Kin auri Jaheed kika sace kanki sannan kika zo kika auri Abubakar"
"Baka da hankali"
"Nagode"nace da ita sannan naci gaba "na biyu kin kashe Auwal sai kuma Laila da saurayinta sannan sai masu gadin ministry inda kika kashe daya sannan kika raunata daya sai kuma Hajiya Jummai. Hadiza wallahi ko kadan baki da imani yanzu duk tsufa da kyautatawa irin na wannan matar amma baki 'kyaleta ba,wacce irin zuciya ce dake. Sai kuma na bakwai ma'aikacinki da kika kad'e a mota"
"Ka gama 'kirgen?
"Eh"
"Ina fa ka gama,ai baka lissafa da kanka ba"
.
Sosai na tsorata ban san lokacin da fitsari ya d'isomin ba,bawai mutuwar nake tsoro ba sai dai yanayin yadda ta furta hakan ya nuna zan sha wahala.
"Hadiza"nace da ita
"Fad'I"
"Wai kuwa kin yarda da Allah?"
"Kar ka dameni da shirmen banza,duniyar nan da kake gani wayonka da 'karfinka ne zasu kwaceka"
'Kura mata ido nayi na 'yan wasu da'ki'kai sannan na dora da cewa "me yasa tun fari baki kashe ni ba kika zo kina kashe wa'dannan bayin Allah,ko kinsan cewa da farko kin kashe ni shikenan karshen tashin hankali kenan."
"Ji nayi a jikina cewa kasan ina biye da kai shi yasa ban yi yun'kurin afka maka ba saboda nasan zaka iya zama cikin shirin haka,kaga idan na gwada afka ma ban samu nasara ba shikenan asiri na ya tonu suma sauran da kaga na kashesu shammatarsu nayi saboda basu ta'ba kawowa a kansu zan kashe su ba. Lokaci d'aya ne nayi yun'kurin take ka da mota amma sakamakon gosulo da cinkoso na mutane tasa na gudu na bar motar"
"A'a ba wannan kad'ai bane,kin manta da tarkon da kika had'amin da dutsin guga (iron) lokacinda kika gayyaceni gidanki?"
"Kwarai kuwa sai dai wannan nima nasan ba lallai plan d'innawa yayi aiki ba"
"Yauwa wannan ne ma ya tunamin da wani abu da masu pidgin english ke cewa man miss road. Babu shakka mutane kamarki wad'anda suka kasa gano baiwar da Allah ya musu suke kasancewa cikin 'dayan biyu ko dai kiga sun dauwama cikin talauci ko kuma su azurta kansu ta mummunar hanya"
"Kana nufin ni yanzu ban gano baiwar da Allah yamin ba kenan?"
"Kwarai kuwa,irin yadda kika nuna rashin saninki a lokacinda na nuna miki 'bud'add'iyar wayar dutsin babu wanda zai gano da gangan kikayi. Da ace zaki shiga shirin film tabbas sai kin zamo best actress"
"Hmmm na sani amma dai bana dana sanin kasancewata haka"
Da alama duk wasu abubuwa da nake son fad'amata don siyan lokaci sun fara 'karemin,hakan tasa na zura mata ido ina kallonta a yayinda 'kwa'kwalwata tayi nisa a duniyar tunani
"Yauwa wai kuwa ya akayi kika san ina bincike a kanki?"
"Hmm baka san cewa ni 'yan biyu bace?"
"Fadamin yadda akai kika gano"
"Tun a tattaunawarmu na sha jinin jikina cewa akwai dalilin da ya kawoka wajena na sani jaridar da ka buga ko kuma ka bawa wani ya buga akan tattaunawarmu kayi hakane bawai don makaranta ba sai dan ka kawar da tunanina. Sai kuma mafarki da nayi kwana daya kafin a koreka a aiki,a mafarkin na ganka ka biyoni da gudu hannunka rike da wuka tsirara. Nayi 'kokarin guje maka amma na kasa duk inda nayi sai ka bini a haka har nazo kan wani tudu wanda 'kasansa ruwa ne da duwatsu na rasa yadda zanyi kai kuma gashi kayiyo kaina gadan-gadan ganin haka yasa na zabi fadawa kasan tudun. 'Karar da na saki ce ta farkar dani daga baccin da nake,sosai na tsorata da mafarkin kuma na tabbatarwa kaina cewa kana bincika ta hakan tasa washe gari na tafi ma'aikatarku anan na sami wani nake tambayarsa game da kai shine yake fad'amin ai an kore ka. Na tamabayi dalilin da yasa aka koreka sai ya cemin wai yaji cewa kana son bincikar wata mata a Khairat Night Club maigidanku ya hanaka amma ka 'ki har kaje gidan mutumin da gawar matar take. Shine ma ya bani adreshin gidanka"
Tunani wanda ya san adreshina a ma'aikatarmu ne ya fad'omin sai kuma na tuna da cewa ashe fa bamu da yawanda zamu kasa sanin juna
"Daga nan sai na wuce gidanka kai tsaye cikin sa'a sai na iske kana fitowa daga ciki d'auke da jaka a hannunka alamar zaka bar garin. Sai da na bika har tashar motar inda naga kahau motar Jigawa-hadejia ganin haka tasa na juyo sannan na watsar da lamarin domin ban kawo kaina saboda ni zaka can ba sai kuma daga baya mafarkin yayi ta zuwamin daga nan kuma na fara bibiyarka"
"Dakyau! Ina ma nima ina da irin wannan baiwar. Kafin ki kashe ni ina son zan roki wata alfarma a wajenki"
"Ina jinka"
"Don Allah ki dawo min da rediyota da dubu na d'aya da kika dauka a gidana saboda 'yan uwana su gada

TSEGUMI 14

TSEGUMI-14
.
A gida ne dana dawo na gwada finger prints d'in kwalbar turaren da na bata ta ri'ke. Ganin sunyi matching da sauran,yasa raina yayi fari saboda na tabbata kwanannan zan binciko sirrin da idan har nayi nasara zan zamo 'daya daga cikin manya wa'danda ake ji dasu a duniyar bincike da jarida sai dai ina ji a jikina akwai abu guda daya kamata na gano kafin ha'ka ta ta cimma ruwa. Ban'daki na wuce kai tsaye na watsa ruwa bayan na fito ne na kimtsa kaina cikin wasu 'kananan kaya sannan na 'dauko 'yar 'karamar bindigar da na aro na cusata a tsakanin bel da wandon da na 'daura. Duk da kasancewar dare ne ko kad'an ban ji tsoron fita ba a daidai wannan lokacin saboda ina tunanin wannan shine mafi cancantar lokacin da ya kamata na isa wurin
Hanyar Zaria na nufa cikin matsanancin gudu,sai dai na kasa kwantar da hankalina sakamakon hangen bayana ta mirror da nake ko zan hangi mutumin da ke bibiyata na biye dani wannan karon ma,amma banga alamarsa ba. Tunanin zan iya wuce wajen ne sakamakon masifaffen gudun da nake ya sani rage tafiyar da nake har na isa wuri. A gefe na ajiye motar sannan na kutsa kaina gidan gonar cikin matsanancin duhun daren,tsoro ne ya ziyarci zuciyata. Tsintar kaina nayi ina waige-waigen bayana kar aljani ya fito min amma shiru,sai a sannan kuma na tuna da bindigar da ke ma'kale a 'kuguna. Wani 'karin kuzari naji yazomin cikin ta'kama da kwanciyar hanakali na durfafi ginin da ke tsakiyar gonar ta hanyar bin wata 'yar siririyar hanya. Da farko nayi niyyar kunna 'yar 'karamar tocilar da ke jikin wayata amma sakamakon bana so mutane su hangi hasken daga titi ya sani kauda wannan tunani har sai na isa ginin.
A kulle na iske 'kofar shiga ciki sai dai ban sha wahala ba wajen bud'e 'kofar domin tuni na 'kware wajen bud'e irin 'kofofin. Sai a sannan na kunna fitilar wayar ina haskaka kowanne sashe na d'akin, a gefen haguna na hangi wata makekiyar akwati ta katako ajiye a 'kasa. Idan ka 'dauke akwatin babu komai a d'akin sai taga dake 'daya sashen na 'dakin suna fuskantar juna da kofa. Akwatin na nufa da niyyar bud'eta amma sai na isketa a kulle da wani 'katon 'kwad'o,na jima kana nasha wahala kafin na samu damar bud'e kwad'on. Wani wari ne ya ziyarci hancina lokacinda na bud'e ,'kwarangal 'din mutum ne shimfid'e a ciki babu ta yadda za'ai ka gane ko wanene. Tun daga 'kafa na fara haska 'kwarangal d'in har zuwa kansa,a daidai goshinsa tsakanin kwarmin idanunsa biyu wani d'an rami ne wanda na tabbatar da cewa na harsashine da aka harbeshi dashi. Tunanin irin rama wula'kanci da cin mutuncin da ubangidana (Ibrahim Atiku) yamin ne ya sani mursmushi ganin yadda na binciko abinda yake tunanin ba mai yiwuwa bane. Tabbas yanzu kam na gama warware komai da 'kwararan hujjoji.
Kamar yadda na saba ji a jikina yawancin lokuta idan wani na kallona,haka yanzunma nake ji kamar da mutum a bayana. Waigowar da zanyi yayi dadidai da lokacinda aka kunna 'kwan lantarkin da ke 'dakin hakan ta sani sakin murfin akwatin da 'karfi ta koma ta rufe. Mutumin da ke bibiyata ne tsaye a bakin 'kofar hannunsa ri'ke da bindiga yayi shiga cikin ba'ka'ken kaya kamar dai yadda na ganshi lokacin da na fito a 'dakin Laila sai dai wannan karon babu ba'kin gilas a idanunsa.
.
Sosai na tsorata da yananyinsa musamman ganin yadda ya saita bindigar tasa 'kirjina saitin zuciya,ko kad'an babu alamar annuri ko fara'a a tattare dashi hakanne tasa na 'kara tabbatarwa da kaina ba lalle na sha ba. Bayan na mi'ke tsaye ne had'e da d'aga hannuwana sama alamar surrender sai naji tsoron da ke zuciyata ya kau,tsintar kaina nayi ina mai cewa "Hajiya Fatima Jaheed,babu shakka dama ina tsammaninki nasani kina biye dani da fitilar motarki a kashe,kin kusa makara domin tuni har na gama abinda ya kawoni ina shirin fita kika risken"
"Da ni kai ne,to tabbas da tuni na fara bankwana da duniya domin babu makawa yau d'innan sai na kashe ka"tace dani
"Na sani"nace da ita. 'Kwa'kwalwata ce ta fara aikin neman mafita kafin daga bisani na 'dora da cewa
"Kafin ki kashe ni zan so ki bani damar fadar wasu abubuwa"
Tsawon wasu da'ki'kai bata ce dani 'kala ba sai ma zubamin na mujiya da tayi idanunta basa ko 'kiftawa daga kaina daga bisani ta numfasa had'e da cewa "ina jinka,amma ka tabbatar ka ta'kaita domin tuni na fara 'kaguwa na kasheka"
"Kar ki damu,zaki cika burinki a kaina kafin gari ya waye"
"Ya isheka haka,ka fad'I abinda kake son fad'a ko kuma yanzunnan na aika ka lahira"
"To!"Nace da ita a lokacinda na jingina da jikin bango idanuna a 'kasa suna kallon wajenda na ajiye bindiga ta,sai dai na tabbata bani damar 'daukota sakamakon attacking d'ina da tayi. Babu shakka ya kamata na siyowa kaina lokaci don haka nema yasa na fara daga farko a lokacinda na d'ago kaina ina kallonta.
"Labarin na da tsayi,zanso kiyi min uzurin sauraro"
"Babu ruwana da tsayinsa,kasan yadda zakayi ka maidashi gajere"
"To! Shekaru uku da suka shud'e akwai wani abokina dake garin kaduna daya ta'ba gayyatata 'daurin auren kawunsa Alhaji Jaheed Auwal na tabbata kinsan abokinnawa. A wajen 'daurin auren naku ne na ganki anan naji sunanki Fatima. Bayan watanni uku kuma da aurennaku sai na samu labari a kafafen yad'a labaru cewa an sace ki sannan aka bu'kaci makuden kud'ad'e a wajen mijinnaki kimanin miliyan goma saboda tsabar yana sonki shi kuma ya biya kud'in amma duk da haka suka kasheki sai gawarki ya tsinta. Satinnai biyu da suka gabata kuma na kai ziyara Khairat Night Club to ananne kuma na ganki. Da farko kasa gano wajenda na sanki nayi sai daga baya bayan na 'karasa gida. Naso na gamsar da zuciyata cewa ba ke d'in bace saboda na san ba'a mutuwa a dawo amma na kasa"
Duk wad'annan surutan banzan da nake cikata dasu ina yinsu ne domin siyawa kaina lokaci,a zuciyata ina Allah-Allah na samu hanyar da zan kubuta. Shi yasa ma na raba hankalina gida biyu 'daya ina amfani dashi wajen surutan a yayinda 'dayan kuma ya shiga searching (binciken) mafita
"sai ku...."Shiru nayi a lokacin da naga ta baro jikin 'kofar sannan ta 'kara taku biyu zuwa sashena sannan ta tsaya
"Muje"
Babu shakka na lura da cewa tana son taji labarin ko dan ta san ta yadda akai na ganota ko dan tabi ta toshe duk wasu hanyoyi da nabi wajen ganota saboda gaba bayan ta kasheni
"Yauwa kamar yadda na fad'amiki zuciyata ce ke ingizani take rayamin cewa kece Fatima Jaheed wannan dalilin yasa na kira ubangidana nake fad'amar amma sai yake fad'amin cewa ba ke bace domin Fatima Jaheed an kasheta kuma har yanzu gawarki na gidansa a ajiye. Ko kad'an ban gamsu da abinda ya fad'amin ba,hakan tasa na yanke shawarar zuwa gidan Jaheed 'din ganin gawar. Yau kwana sha uku kenan da zuwana gidan ganin gawar sai dai nayi rashin sa'a Jaheed ya kamani a gidan. Na tsorata sosai lokacin hakan tasa na fad'amasa dalilin zuwana gidannasa. Maimakon ya dam'kani ga 'yan sanda ko kotu sai yace dani ya bani sati biyu (kwanaki goma sha hudu) na tabbatarwa duniya cewa kece matarsa ta asali. A lokacin ni kaina nasan hakan ba mai yiwuwa bane amma duk da haka ban karaya ba na fara bincike a kanki,ko zaki so kiji yadda na gudanar da binciken?"
"Ina jinka"
'Dakin nake 'karewa kallo,babu komai a cikinsa da zai taimakmin wajen kare kaina. Takaici ne ya ziyarci zuciyata ko kad'an ba mutuwar nake tsoro ba amma ace wai macece ta kasheni abin da ciwo gaskiya kuma na tabbata irin kisan wula'kancinnan zatamin mafi muni.
"Ci gaba mana"tace dani
"Da farko zan warware basajar da kikayi kece Hadiza Abdullahi Adamri wannan shine asalin sunanki ba Jamila ko Fatima ba sannan ke 'yan biyu ce. Sunan 'yar uwarki Zainab Abdullahi Adamri. Kuna matu'kar kama da juna sannan ku kad'ai iyayenku suka mallaka wad'anda suka mutu sanadiyyar hatsarin mota. Kun taso baku san kowa ba a danginku hakan tasa wata ma'kociyarku Hajiya Jummai taci gaba da ri'ke ku amma saboda rashin godiya irin taki kika gudu da 'yaruwaki kuka barta. Bayan kun gudu ne daga baya kowaccenku ta kama gabanta,inda ke kika had'u da Abubakar Garba kuka fara soyayya duk da kasancewarsa 'dan iska zauna gari banza. Daga baya kuma kika had'u da Jaheed Auwal a 'daya daga cikin restaurant 'dinda kikai aiki ya nuna yana sonki kika amince ba wai don ke kina sonsa ba sai don wani dalili naki da ke kad'ai kika barwa kanki sani. Daga baya kuma kika shirya wani plan 'dinki da Abubakar inda kika aiko masa daya je gidan karuwai ya duba Zainab ko tana nan,bayan ya dubo ya fad'amiki shine kika taho daga kaduna kika tafi da'ita wajensa (Abubakar) kuka 'boyeta sannan kika sace kanki a matsayin 'barayi ne suka saceki da had'in bakin Abubakar kuka aikawa Jaheed akan idan yana son a dawo masa dake sai ya biya miliyan goma shi kuma saboda tsantsar begenki da yake ya biya kud'in ku kuma sai kuka kashe Zainab 'yar uwarki kuka ajiye masa gawarta yazo ya dauka a tunaninsa ke ce sakamakon matsananciyar kamannin da kukayi. Ya kika ce gameda bincike na?"
"Kai Karshe ne a duniyar Jarida da bincike"tace dani
Murmushi ne ya su'buce min jin wannan sunan da ta kirani dashi
"Au wai murna kake don na kira ka da haka? To ka daina,wai ma tsaya kanajin akwai wani mutum mai hankali da zai gamsu da duk wad'annan 'kir'kirarrun labarin da ka tsara?"
"Alkali zai yarda da batuna domin kuwa ina da hujjoji"
"Wanne Alkalin?"
"Na kotu man"
"Yimin shiru ! Ai yanzu haka kana kotunda daga nan sai lahira"!!!!www

TSEGUMI 13

TSEGUMI-13
.
"Kayi hakuri zan turo wani yanzu ya tayaka canja wata tayar"
"Babu komai,nagode"
"Sai da safe"
"Allah ya tashemu lafiya"nace daita. Har tayi nisa ta dawo "Dan Allah idan bazaka damuba mu had'u a gidana mana gobe"
"Ba damuwa Allah ya kaimu goben"bayan ta ban adreshin gidan ta juya taci gaba da tafiya. Ranar ban isa gida ba sai misalin 'karfe daya da rabi na dare (01:30am).
Washe gari a zuciyata na yanke shawarar zuwa kaduna gidan Jaheed Auwal bayan na biya ta gidan Jamila kamar yadda ta nemi naje. A hanya nake ta nazarin dalilin da zai sa tace nazo gidanta. 'Kwan'kwasa 'kofar gidan da ta kwatantamin nayi ina jiran a bud'e amma sai naji ance shigo. A ciki na isketa da 'kananan kaya na training tana faman press up. Bata ko kalleni ba taci gaba da abinta,nima ban kulata ba sai ma 'karewa 'dakin kallo da nake a lokacin da na rufe kofar. 'Katoto ne 'dakin wanda girmansa zai linka girman normal daki sau biyu,a can wani lungu irin 'katon table "dinnan ne na snooker a 'daya sashen kuma makekiyar rediyo ce a jingine da bango. Idan ka 'dauke wa'dannan abubuwan to babu komai a ciki. Bayan na gama 'karewa 'dakin kallo ne na dawo da hankalina gareta na fara 'kirga press up 'din da take,sai da na 'kirga arba'in sannan ta tashi.
"Dakyau! Kina 'ko'kari fa,kinyi ya kai arba'in"
"Saba'in nayi"tace dani tana haki
"Ya kake?"
"Lafiya lau"
"Kullum kike wannan press up d'in?"
"A'a ina yi sau biyu a sati,ka iya snooker?"Tace dani lokacinda ta nufi wajen snooker
"A'a ban iya ba,sai dai in zaki koyamin"
Nan fa ta fara tarwatsa balabalannan tana jefasu a rami,babu shakka ta 'kware a wannan fannin ma. Bayan ta gama jefasu ne ta duba agogon hannunta "La'ila" kaga har na kusan makara ma akan abinda nake so zamuyi dakai. "Biyoni"tace dani
"Ina so ne kaban shawara akan fara kasuwancin Jarida"tace dani a lokacinda muka shigo wani 'daki mai kama da dressing room. "Ina so ne nima na bud'e ma'aikata tawa ta jarida"
"Me da me kike son sani gameda harkar?"
Dutsin guga ta 'dauka ta jona a jikin socket sannan ta fara goge kayanta a kan wani benci mai fad'I lullu'be da yadi. "Komai ma"
Nan na fara mata bayanin ta yadda zata fara da irin aubuwan da zata tanada har ta gama goge rigar sannan ta 'dauko skirt zata goge
"Don Allah taimaka ka gogemin skirt 'dinnan man zan shiga wanka,idan na dawo maci gaba"
Kafin na bud'e bakina har ta fice daga 'dakin. Wuta ce ta jani a lokacinda na kama iron (dutsin guga) 'din sai a sannan na lura da wayar jikin iron 'din ta sille kamar wacce 'bera yaci. Ajiye dutsin da kayan nayi na koma gefe na tsaya. Bayan wasu 'yan mintina sai gata ta dawo
"'Kin gogemin kayi ko?"
"Tarko ne wannan"nace da ita
"Tarko !Kamar ya tarko me kake nufi?"Tace dani a lokacinda take 'ko'karin kama iron 'din
"Dakata"
"Me ya faru?"
A hankali na dauki iron 'din na nuna mata wajenda wayar ya sille
"Tab! Allah ya taimakeni,kai amma nagode da ka ceci rayuwata Haidar"
"Babu komai,mu ci gaba da tattaunawarmu kawai"
"Mu bari sai wani lokacin maci gaba wallahi gaba daya na tsorata"
"Kar ki damu lokacinki baiyi ba tukun,zan wuce ni saboda ina so zanje kaduna yau"
"To shikenan nagode"
"Amma akwai 'bera a nan ne?"
"Akwai su"
"Ya kamata ki nemi maganinsu"
"Zanyi 'ko'karin hakan".
A hanya nake ta tunanin yadda akai ta goge rigar ba tare da iron 'din ya ja ta ba a karo na farko. Na tabbata yadda na kama dutsin gugar haka kowanne irin mutum zai yi idan ya tashi guga. Ya kamata ace itama dutsen ya ja ta a karo na farko.
Misalin sha 'daya na isa garin,kai tsaye wajen abokina daya gayyaceni auren Jaheed na wuce. Bayan mun gaisa na 'dan huta nake tambayarsa gameda Jaheed
"Wai ya labarin kawunnannaka yana nan?"
"Yana nan,gobe ma zamuje 'kauye ta'aziyya nida shi"
"Ok! A goben kuma zaku dawo?"
"A'a sai mun kwana biyu gaskiya"
Naji da'din haka domin ina son le'kawa gidannasa don 'karasa wasu bincike sai dai na yanke shawarar komawa kano yau don gudanar da wani aiki a Khairat Night Club kafin goben na dawo. Ban kama hanyar dawowa gida ba sai misalin shida na yamma,na isa kano da daddare misalin karfe tara. Kai tsaye Khairat na wuce sai dai wannan karon shiru na iske wajen sa'banin sauran lokuta da zakaji ki'de-'kide na tashi da tulin mutanen na 'dud'd'ukuwa ciki,a hanakali na'karasa wajen masu gadin zuciyata na bugawa.
"Barkanku da yamma"
"Yauw barka dai"
"Meke faruwa anan ne?"
"Yau bama aiki,mun rufe sakamakon bige wani abokin aikinmu da akayi yau a mota"
"Wanene?"
"Ba zaka sanshi ba"
"Kwatantamin yanayinsa"
A irin yadda ya siffantamin shi na tabbatarwa kaina cewa saurayinda nasa ya kula da shiga da ficen Jamila ne aka kad'e.
"Amma taya har aka buge shi?"
"Yau ne da safe zai koma gida a kan hanya"
"To yazo tsallaka titi ne ko ya?"
"Ko 'daya a gefen titi ma yake tafiya"
"Ina Jamila?"
"Kana nufin Hajiya?"
"Eh"
"Ta koma gida"
Haka nima na koma gida zuciyata cike da takaici da tunani!!!
.
Ban kama hanyar kaduna ba sai da la'asar sakaliyarta,wannan karon na yanke shawarar tunkarar maigadin kai tsaye yayin shiga gidan saboda zanfi samun nutsuwa da kwanciyar hankali wajen gudanar da abinda nake son aiwatarwa a gidan kasancewar maigidan baya nan kamar yadda abokina ya fad'amin,yau ne zasuyi tafiya,na tabbata yanzu kam sun bar garin. Bayan sallar magriba na isa kofar gidan kai tsaye wajen maigadin na nufa na masa sallama sannan na fara tambayarsa.
"Ka gane ni kuwa baba?"
'Kuramin ido kawai yayi yana nazarin fuskata a 'ko'karinsa na gano wajenda ya sanni na 'yan wasu dakikai kana ya numfasa hade da cewa
"Eh to kamar dai na shaida ka,amma ban wayeka ba sosai"
"Ka tuna kwanakinnan da suka shu'de da daddare maigidanka ya saka ka fita dani zuwa 'kofar gida?"
"Ok ! Na ganoka kuma"
"Yauwa !Ya fadama abinda ya kawoni kuwa waccan lokacin?"
"A'a bai fadamin ba,me ya faru?"
"Wato abinda ya kawoni waccan lokacin shine wata mata na gani da sukai matu'kar kama da matarsa da aka kashe,tsantsar kamannin da sukayi ne ya sani yanke shawarar zuwa naga gawar matar tasa ko itace ta rayo shine ya kamani. kaji dalilin zuwana waccan lokacin"
"Dama ana mutuwa a dawo?"
"Eh to ance dai wai wasu suna yin fatalwa su dawo"
"Amma yanzun dai ina fata ba wajen gawar ka sake dawowa ba?"
"Wajenta nazo"
"Ba zai yoyu ba gaskiya"
"Saboda me?"Nace dashi a lokacinda na zaro dubu 'daya na dam'ka masa a hannun
"Saboda babu mukullin gidan a wajena"
"Kar ka damu zan san yadda zanyi na shiga"
"Amma ina fata bazaka jima ba?"
"Minti goma sha biyar ma ya isheni zan gama abinda zanyi na fito"
"To yanzu yadda za'ayi ka koma wani wajen ni kuma zan je na kashe fitulun gidan sai ka dawo"
"To ba damuwa"
Bayan naga ya kashe gaba d'aya fitulun gidannane na shigo,kai tsaye 'dakin da gawar take na nufa. Bayan na bud'e gilashin da take ciki na 'dauko camerar da na aro agun abokin aikina na fara daukarta a hoto. A hankali na maida na rufe gilas 'din kamar yadda yake da sannan na shige 'daya daga cikin sauran 'dakuna ukun dake gidan,ina shiga na tabbatar ba shine 'dakin da nake nema ba don haka na fito daga ciki na fad'a 'daya 'dakin. Babu shakka wannan shine 'dakin Fatima sakamakon tulin kayan matan dana gani a cikin wani wardrobe dana bude,sai kuma jibgin turararruka da na gani da sauran kayan shafe-shafe na mata akan dressing mirror. Wata 'yar 'karamar leda na zaro daga aljihuna na 'dure wasu daga cikin kwalaben turaren ta hanyar amfani da hankici sannan na zurasu cikin aljihuna na wando. Ci gaba nayi da bincika 'dakin anan naga wani photo album na bikinnasu cikin wata loka dake jikin dressing mirror 'din. Sai da na zabi hotonta da nake ganin shine yafi miin sannan zai taimakamin wajen gudanar da bincikena shima na cusashi a aljihun wandona na 'daya 'bangaren sannan na fito daga cikin gida.
"Baba kaga ban jima ba ko?"Nace da maigadin a lokacin da na fito daga cikin gidan
"Eh baka jima ba kam"
"Yauwa nagode ni zan koma"
"To madallah, Allah ya kiyaye hanya"
"Ameen"
A gida ne na 'dauko hotuna biyun ina nazarinsu. Na jima ina kallonsu irin kallonnan da ake kira na 'kurilla amma ban ga wani bambanci ba tsakaninsu. Tabbas da ace zasu saka kaya iri 'daya to bazaka iya bambancesu da juna ba. Sake dawo da dubana nayi jikin hoton daga sama zuwa 'kasa a karo na ashirin sai a sannanne naga wani abu daya ja hankalina,akwai'dison ba'ki 'dan 'karami jikin kunnen hoton da na sato a jikin photo album 'din kusa da wajenda take ma'kala 'dan kunne sa'banin na Zainab. Finger prints gadget na 'dauko sannan na fara gwada sauran kayayyakin anan nayi compairing 'dinsu dana agogon da na gani a motar da ke bibiyata. Nayi matu'kar mamaki ganin yadda sukayi matching.
Washe gari da safe na isa Khairat a ciki na iske matar da tamin iso kwanaki nake tambayarta Jamila
"Hajiya bata nan"
"Amma zata zo office yau?"
"Ban sani ba gaskiya,har yanzu tana jimamin mutuwar abokin aikinmu ne"
"Zan le'ko zuwa anjima da daddare ko zata zo"
"To"
A hanya ina dawowa gida na biya ta wani shago da ake sai da turare na sayi 'kwalba daya 'karami na sashi a aljihu na wuce gida huce gajiya kafin daren yayi.
Tun da misalin 'karfe tara na dare na isa can amma dana tamabayi masu gadin ko sun ga shigowarta suka ce bata zo ba. Ciki na wuce sannan na samu waje na zauna ina jiran 'karasowarta. Har sha 'daya da rabi ta gota amma bata 'karaso ba hakan tasa na tashi zuwa wajen matar naji ko Hajiyan zata zo yau
"Banajin zata zo gaskiya,amma dai ka jirata"
"Ba matsala na dawo gobe kawai dama jaje nazo yi mata"sannan na fito da niyyar fita sai kuma na hangota tana shigowa.
"Hajiya sannu da shigowa"
"Yauwa Haidar"
"Ya aka ji da hakuri kuma?"
"Alhmdulillah"
"Ai na jima ina jiranki na jajanta miki bakya nan"
"Eh wallahi,ina gida kasan na matu'kar ji takaicin abun"
"Sai ha'kuri"
"Naso ace masu gadin sun rike lambar motar wallahi da sai mun shiga kotu dashi"
"Ba mamaki direban 'danye ne ko kuma........Wai
yo Allah idona"na 'kwala da 'karfi ina murstika ido
"Me ya faru?"
"Ri'kemin"na mi'ka mata 'walbar turaren da na siyo sannan na fara goge idon nawa da hankici
"'Kwaro ne ya fadama?"
"Inajin 'kwaro ne"
"Ya fita"
"Eh ya fita"
"To Allah ya kiyaye bari na 'karasa office nagode"tace dani sannan ta mi'komin kwalbar turaren. Sai da na rufe hannuna da hankicin sannan na 'kar'bi kwalbar

TSEGUMI 12

TSEGUMI-12
.
Tunanin bincika gidajen karuwai dake garin (kano) ne ya zomin ko zan dace na sameta. Ni kaina nasan ban isa na gama gewaye gidajen karuwan da ke fadin garin ba ko da tsawon shekara zan shafe inayi amma duk da haka ban karaya ba na fara bi daga nan zuwa can amma ban dace ba. Na zaga gidajen karuwai a 'kalla sama da 'dari biyu sai a wanine na samu wata nake tambayarta.
"Kinga tambayarki kawai zanyi sannan na biyaki ba wani abu ne ya kawo ni ba"
"Tambaya?"
"Eh"
"To ina jinka"
"Wata yarinya Zainab Abdullahi Adamri nake tambaya ko kin santa?"
"Zainab ta bar nan"
"Kika ce me?"
"Nace ta bar nan"
"Kin santa?"
"Eh sosai ma"
"Ya kuke da ita?"
"'Kawata ce"
"Kenan bazaki rasa hotonta ba ko?"
"A'a amma dai mun ta'ba dauka sai dai har yanzu bamu karbo ba agun mai hoton"
"Ina wajen hoton?"
"Anan unguwar ne"
"Ya sunan wajen"
"Al'ameen professional photos"
"Amma kinsan inda ta koma"
"A'a"
"Kika ce 'kawarki ce?"
"Eh,lokacinda ta tafi bana nan da na dawo ban ganta ba nake tambayar 'kawayena suka cemin ai wata tazo ta tafi da ita. Sun ce suna matu'kar kama da juna 'kila ko 'yar uwarta ce"
"Tun yaushe ne hakan ya faru?"
"Shekaru uku kenan yanzu"
Bayan na sallameta na koma mota. Na 'dan 'dauki lokaci ina zazzagawa kafin daga bisani naga shagon mai hoton amma a rufe. Washe gari da safe na koma shagon wannan karon a bud'e na samehi,kutsa kaina nayi ciki
"Malam barka da aiki"nace da saurayin da na iske a shagon
"Yauwa,sannu da zuwa"
"Akwai wata yarinya da ta'ba daukar hoto anan"
"Wacce yarinya fa?"
"Sunanta Zainab Abdullahi Adamri"
"Zainab ? Kai na mantata gaskiya"
"Karuwa ce anan kusa da ku take ta jima da 'daukan hoton"
"Ok ! Na tuna kuma"
"Hotunan da ka 'dauketa nake so zan siya"
"Hhhh ai ta had'u yarinyar bari na 'dubosu"yace dani yana dariya a lokacinda ya shiga wani daki. Bayan wasu 'yan dakikai ya dawo rike da hotunan a hannu
"Yauwa gasu ko,sai ka zaba"
Basu da wani bambanci da Fatima Jaheed haka Jamila ma. Yanzu kam na fara warware abubuwan amma matsalar wajenda zan had'u da Zainab 'din. Ko dai Jamilar ce ta canja sunanta daga Zainab zuwa jamila? Amma kuma banajin Jamilar itace Zainab saboda bambancin halinsu halayenta yafi kama dana Hadiza kamar yadda bincikena ya nuna min. Idan kuma Jamilar itace Zainab a ina ta samu ku'din da zata gina kanta haka sai sannan kuma na tuna ashe fa tace dukiyar mijinta ta gada. Shi kuma a ina ya tara wannan dukiyar? Shima ai bincikena sun nuna matsiyaci ne. Dole shima na zurafafa bincikena a kansa,wannan dalilin ne ya sani ci gaba da ziyartar sauran mutanen da ke jikin takardar da na samo a kamfanin takalma.
"Abubakar abokina ne sai dai mun daina ganin juna tun shekaru uku da suka wuce"wani abokinsa dana kaiwa ziyara yace dani wanda shima sunansa na jikin takardar
"To lokacin a ina yake da zama?"
"A gyadi-gyadi yake"
"Amma me yasa kuka daina ganin juna?"
"Haka kawai na daina ganinsa"
"Nagode"nace dashi sannan na nufi gyadi-gyadi har gidan da ya kwatantamin amma sai na iskeshi a rushe. Wajen wani mai shago na 'karasa kusa da gidan nake tambayarsa
"Malam yaushe ginin nan ya rushe?"
"Yau shekara uku kenan"
"Nagode"nace dashi sannan na koma mota. Har na tayar da ita ina shirin tafiya na tuno da wani abu. Rusasshen ginin na nufa,anan na sunkuya ina binciken abubuwa da ni kaina ban san me nake nema ba sai kace mahaukaci. Wata tsohuwar dirowa na gani bayan na jawo ta kusa dani ne na fara binciken abubuwan da ke ciki. A ciki ne naga wata 'yar 'karamar takarda da rubutu a jikinta kamar haka
Zuwa ga Abubakar
Na rubuto na sanar dakai cewa abubuwa sun daidaita kuma zan so na sani ko ka bincika wannan abun kamar yadda na fadama idan bakayi ba don Allah kayi 'kokari kayi kaga lokaci na 'kuratowa kuma abin nada muhimmanci. Ashirin ga wannan watan zan taho saboda zai fita kasuwanci na 'yan wasu kwanaki. Amma ba zanzo wajenka ba saboda bana so mutane su ganeni mu had'u a can wajen gari hanyar kazaure gaba da bandirawo city. Sai anjima
Daga masoyiyarka
Hadiza.
PLS!!! Kar ka kuskura kace zaka kirani ko kace zaka zo ko ka rubutomin wasika. Ka bari ni zan shirya komai.!!!!
.
Nannad'e takardar nayi na totsata a gaban aljihun rigata sannan naci gaba da bincika sauran takarcen dake rusashshen gidan amma ban samu wani abu mai muhimmanci ba. Hakan ta sani dawowa cikin mota sannan na nufi gida da niyyar hutawa kafin dare yayi na le'ka Khairat Night Club.
Misalin takwas daidai na dare (08:00pm) na kama hanyar Khairat,nesa dani daga baya na hango wasu motoci guda biyu na taxi na biye dani a raina ina tunanin yaran Jaheed ne dake biye dani,wannan karon ban damu da duba lambar motocin ba domin nasan su 'dinma na haya ne. Fakin 'din motar nayi a wajen da aka tanada saboda ajiye motoci a club 'din sannan na shige ciki. Wannan saurayin ne ya sake tarbata wannan karonma.
"Sannu da dawowa yallabai"yace dani
"Yauwa"
"Wannan karon me kake da bukata ko giyar?"
"A'a Maltina nake so"bayan ya kawomin ya juya da niyyar komawa na sake kiransa
"Don Allah inaso zan maka wasu tambayoyi idan bazaka damu ba"
"Ba matsala amma sai dai zuwa anjima misalin sha biyu (12:00pm) kafinnan aiki yayi sau'ki"
"Ba damuwa ina nan har zuwa lokacin"nace dashi. Tashi nayi ina 'dan zazzagawa har wajen matar da min iso wajen Jamila kwanaki.
"Sannunki da aiki"
"Waye kai?"Tace dani a fusace
"Nine 'dan jaridannan na kwanaki da yazo wajen Hajiya!baki ganeni ba?"
"Me kuma kake so yanzu agunta?"Wannan karonma babu annuri a fuskarta
"Dama tambayarta nake so nayi ko taga Jaridar tattaunawar da mukayi"
"Bata nan"
Ganin ban samu fuska ba a wajenta ya sa ni fita daga sashennata,a hanya ne na kusa kici'bis da ita
"Kaine Haidar Ali dan jaridar nan ko?"Tace dani
"Eh nine Hajiya ya aiki?"
"Da godiya,naga jaridar da ka buga"tace dani tana murmusawa cikin wani salo mai kashe zuciya.
"Yauwa dafatan kinji dadinsa?"
"Sosai ma kuwa"
"Yauwa haka nake so naji dama"nace da ita a lokacinda nake 'kare mata kallo daga sama zuwa 'kasa.
"Bari na wuce office"tace dani sannan ta shige.
Sha 'daya da hamsin (11:50pm) matashin ya dawo ya sameni
"Wato akwai abubuwanda nake so na tambayeka"
"Me dame kake son ka sani?"
"Da farko ina so na san wanene Abubakar Garba?"
"Abubakar shine mijin Hajiya amma ya rasu"
"Tun yaushe ya rasu?"
"Ya 'dan jima gaskiya,tun farko-farkon bud'e wannan gidan"
"Amma kasan ta yadda akai ya mutu?"
"Eh to Hajiya tace mana dai wai jirginsu ne ya nutse a ruwa a hanyarsa ta dawowa daga garinsu"
"Amma ya kake ganin sha'kuwarsu da Hajiya kafin ya rasu,sun ta'ba samun sa'bani?"
"Eh to ba sosai ba,amma dai suna zaune lafiya"
"A irin sa'banin da suke samu ko ka ta'bajin wata kalma da suke furtawa?"
"A'a"
"Ka tuna dai"
shiru yayi na 'yan wasu da'ki'kai da alama tunanin yake sannan ya 'dago kansa
"Eh to akwai lokacin da naji Hajiya tana cemasa wai yana kawo tsoffin abokansa. Shi kuma sai yake ce mata shine fa silar samun komai nasu idan ta matsa mar zai fasa 'kwai kowa yaji"
"Ka tabbata kaji haka da kunnenka?"
"Eh na tabbata"
"To amma wanne 'kwai zai fasa?"
"Ban sani ba"
"To me Hajiyan tace daya fad'I hakan?"
"Shiru kawai tayi batace 'kala ba"
"Tun daga wannan ranar daya fadamata haka sun sake samun sa'bani?"
"Basu sake ba,sai dai ko a gida ban sani ba"
"Bayan wannan gidan sha'katawar akwai wani kasuwanci da Hajiyar ke yi?"
"A'a sai dai tana da gidan gona a hanyar Zaria"
"Wajen ina ne?"
"Da ka kama hanyar a bangaren hannunka na hagu zaka ganshi a ciki da wani gida anan Hajiya take hutawa"
Sai a sannan na tuna tattaunawarmu da ita tace tana sha'awar noma. "Yanzu kasan me zakamin?"Nace dashi
"A'a"
"So nake ka sa mata ido ka lura da duk wasu shiga da ficenta,sai kana fadamin ni kuma zan biya ka kullum idan ka samo min wani bayani kaji"
"Ba matsala"
<<<<<
Tayar motata na tarar a sace,sai da na matsa daf da ita na hangi wata zungureriyar 'kusa cake a gefen tayar rabinta ya nutse a ciki. A fusace na juyo na sami masu gadin ina fad'a akan sakacinsu da har zasu bari wani ya shigo ya huda min taya suna gani amma ga mamakina ko ci kanka basu ce ba sai ma zubamin ido da sukayi hakan kuwa ba 'karamin fusatani yayi ba. Ci gaba nayi da yi musu fad'a a fusace sai kace ni na 'daukesu aiki.
"Haidar"naji an kirani a bayana. Juyawar da zanyi muka had'a ido Hajiya ce
"Me ke faruwa ne?"
"Hava ! Wadannan sokayen masu gadin naki ne man,suna gani wani yazo ya fasa min taya zo fa ki ga yadda aka mata"
"Kayi hakuri don Allah,amma nasan ba laifinsu bane sai dai ko a hanya ka taka 'kusar baka sani ba. Amma na tabbata babu wanda zai shigo nan suna gani"
Ko kad'an ban saurari abinda take fad'a ba gaba d'aya hankalina yana kan kamshin turaren da ke fitowa daga jikinta!!!!